fidelitybank

Ƴan fashin banki sun ci karen su ba babbaka tare da harbe jami’an tsaro a Ekiti

Date:

Wani mumunan fashin banki da aka yi a garin Ikere Ekiti na jihar Ekiti a ranar Laraba da yamma, rahotanni sun ce an kashe mutane biyar ciki har da jami’an tsaro biyu na Amotekun.

An samu labarin cewa ‘yan fashin da suka sanya abin rufe fuska, sun afkawa bankunan kasuwanci da ke kan babbar hanyar garin inda suka bude wuta domin shiga harabar bankunan.

Shedun gani da ido sun ce ‘yan fashin sun ajiye kansu a wurare masu mahimmanci inda suka yi harbi ba kakkautawa har na tsawon sa’a guda, lamarin da ya haifar da firgici da hargitsi a tsakanin mazauna yankin.

Wasu daga cikin wadanda harin ya rutsa da su sun samu harbin bindigar ‘yan fashin ne a lokacin da suke kokarin tserewa zuwa tsira.a

Ƴan fashin da suka rufe fuska, kimanin ashirin, sun shiga garin ne da misalin karfe 4:15 na yamma inda suka yi wa bankunan Odo Oja da Oke-osun fashi a lokaci guda.

Kamar yadda majiyar ta bayyana, sun fara kai hari ne kan kwamandan Ikere na Amotekun Corps da ke kan titin Ise, inda aka ce sun harbe wasu jami’an tsaro kafin su far wa bankunan.

‘Yan fashi da makami sun karya kofofin tsaron bankunan da taimakon dynamite, inda suka yi awon gaba da wasu makudan kudade da ba a tantance ba.

Sai dai kuma kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Ekiti, Sunday Abutu ya kasa samunsa har zuwa lokacin wannan rahoton, saboda ba a amsa kiran waya da sakonnin wayar salula da dama. In ji Daily Post.

A halin da ake ciki kuma, a wata tattaunawa ta wayar tarho, Ogoga na Ikere Ekiti, Oba Adejimi Alagbado ya bayyana kaduwarsa game da lamarin fashin.

Ya ce abin takaici ne ‘yan fashi da makami sun gudanar da aikin na tsawon mintuna da dama ba tare da wata tangarda ba, inda suka tsere duk da kasancewar shingayen binciken sojoji da rundunar ‘yan sanda a garin.

Oba Alagbado ya ce ya tattauna da jami’an tsaro kan lamarin, kuma dole ne a kama wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da gurfanar da su a gaban kuliya.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp