fidelitybank

Ƴan Bindiga sun kashe Sojojin da Ƴan Sanda a Zamfara

Date:

Sojoji uku da ƴan sanda huɗu ne suka mutu a wani harin kwantar ɓauna da ƴan bindiga suka kai musu a lokacin da suke ƙoƙarin tarwatsa ƴan bindigan da suka kai wani hari a Zamfara a ranar Alhamis.

Kwamishinan ƴansanda jihar, Mohammed Dalilan ne ya bayyana hakan, inda ya ce ƴan bindigan sun shirya kai wani hari a wani kamfanin gine-gine da suke aikin titi a jihar.

Ya ce hakan ya sa haɗakar sojoji da ƴansanda suka kai ɗauki, inda aka yi rashin sa’a, ƴan bindigan suka musu kwantar ɓauna, suka buɗe musu wuta.

Kwamishinan ƴansanda ya bayyana cewa jami’an tsaron sun yi ƙoƙarin gaske wajen dakatar da harin.

“Sun yi niyyar zuwa kamfanin Setraco ne domin garkuwa da ma’aikatan kamfanin, da muka samu labari, sai muka tura dakarunmu, ashe sun ɗana musu tarko, inda suka yi kwantar ɓauna suka buɗe musu wuta,” inji shi kamar yadda shafin talabaijin na Channels na intanet ya ruwaito.

Ya ƙara da cewa dakarun sun mayar da martani, inda bayan musayar wuta, sojojin suka samu nasarar dakatar da harin, “amma mun rasa sojoji uku da ƴansanda huɗu.”

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp