Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun kashe wani mutum mai suna Emmanuel Rufus a jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar a hanyar Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko-Edo a jihar, kamar yadda NAN ta ruwaito.
Wata majiya da ta so a sakaya sunanta ta ce wanda abin ya shafa na tafiya ne tare da ‘yan uwansa biyu a cikin wata mota kirar Mercedes-Benz GLK a lokacin da ‘yan bindigar suka fito daga daji suka bude wa motar wuta.
Daya daga cikin wadanda abin ya rutsa da su ya mutu a cikin wannan tsari, yayin da sauran mutanen da ke cikin motar suka tafi da su cikin daji.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Edo, SP Chidi Nwabuzor, wanda ya tabbatar da kisan, ya ce ba batun yin garkuwa da mutane ba ne, illa dai kisan kai ne.
Nwabuzor ya ce, rahoton da jami’in ‘yan sanda reshen yankin Igarra ya fitar ya nuna cewa an ga wani Emmanuel Rufus a kwance a kan titin Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko Edo ta jihar.
Ya ce ‘yan sanda da ’yan banga sun yi tattaki zuwa wurin, inda suka gamu da wanda abin ya faru da harbin bindiga a cikin motar, mai lamba BEN 303 GM.
Kakakin ’yan sandan ya ce daga baya danginsa suka dauki gawar marigayin domin binne shi.
A cewarsa, ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, tare da kokarin cafke wadanda ake zargi da guduwa.