An harbe dan DIG Ibrahim Mamman Tsafe mai ritaya, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Zamfara mai ci.
Aminiya ta fahimci cewa, an kashe dan Tsafe tare da wasu mutane uku a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari garin Tsafe, shelkwatar karamar hukumar Tsafe ta jihar a daren Lahadi.
A baya-bayan nan dai, garin Tsafe da wasu al’ummomi da dama a cikin karamar hukumar sun sha fama da munanan hare-hare da garkuwa da mutane, domin neman kudin fansa.
Watanni biyu da suka gabata an kashe wani mazaunin garin da jami’in kwastam a wasu hare-hare da aka kai a garin.