fidelitybank

Ƴan Bindiga sun hallaka DPO bayan sun kai hari jihar Delta

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane sun kai hari tare da kashe wani DPO na ƴansanda a karamar hukumar Ughelli ta Arewa da ke jihar Delta.

Mai magana da yawun ƴansandan jihar, Bright Edafe, shi ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin, inda ya ce ƴan bindigar sun kuma raunata wani DPO na shiyyar Ororoekpe inda aka garzaya da shi asibiti domin ba shi kulawa.

Edafe ya ce jami’an ƴansandan biyu sun fita samame ne da wasu jami’ai lokacin da ƴan bindigar suka yi musu kwantan-ɓauna, inda ya ce ana ci gaba da bin tsawunsu da nufin kama su.

Kakakin ƴansandan ya kuma ruwaito karya doka da oda a wata karamar hukumar Aniocha ta Arewa na jihar inda matasa suka far wa kayayyaki tare da cinna musu wuta.

A cewarsa, tarzomar ta ɓarke ne bayan lakaɗawa wani mutum duka har ta kai ga mutuwarsa da wani yayi wanda suke zargi da kwace filayen al’umma a yankin.

Wasu jagororin al’umma sun nuna adawa da matakin abin da ya janyo tarzomar da ta yi sanadiyyar ran mutumin.

Edafe ya bayyana cewa an kama mutum uku da ake zargi da aikata laifin kuma ana ci gaba da bincike.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp