Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar hukumar Dan Musa ta jihar Katsina sun ajiye makamansu tare da sakin mutum 16 da suka yi garkuwa da su.
Cikin wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na X, ta ce matakin na cikin wani shiri na ci gaba da karɓar makamai da ficewa daga harkar aikata laifuka wanda rundunar Operation Fasan Yamma ke jagoranta tare da hadin gwiwar hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.
Jagororin ‘yan bindigar da suka miƙa wuya sun haɗa da Kamulu Buzaru da Manore da Nagwaggo da Lalbi da Alhaji Sani da Dogo Baidu da Dogo Nahalle da Abdulkadir Black.
A cewar jami’an tsaron, fitattun ƴanbindigar sun miƙa makamansu ne a ranar 14 ga Yuni, 2025, tare da yin alƙawarin barin aikata laifi da zama lafiya da sauran al’ummomi.
An karɓi makamansu kuma an adana su a karkashin kulawar hukumomi, kamar yadda jami’an tsaron suka tabbatar.
Domin tabbatar da zaman lafiyar, tsoffin ‘yan bindigar sun saki mutum 16 da suka haɗa da mata bakwai da yara tara da suke tsare da su, tare da alƙawarta sakin wasu da dama.
Hukumomin soja sun bayyana cewa bayan wannan mataki, lamarin tsaro a yankin Dan Musa ya daidaita, tare da ci gaba da sanya ido daga dakarun soji don hana sake faruwar rikice-rikice.