fidelitybank

Ƙwalara da cutar Sanƙarau sun kashe mutane 32 a Najeriya – WHO

Date:

Hukumar lafiya ta Duniya (WHO), ta ce, kimanin mutum 922 ne aka bayyana cewa, sun kamu da cutar kwalara ko amai da gudawa a Najeriya, yayin da mutum 32 suka mutu sakamon cutar a shakerar 2023 da muke ciki.

A wani rahoton da WHO ta fitar, ta ce, zuwa 5 ga watan Maris 2023 yawan mace-mace sakamakon cutar ya kai kashi 3.5 cikin 100

WHO ɗin ta kuma ce, alƙaluman sun haɗar da waɗanda suka bayyana alamun cutar, da kuma waɗanda aka tabbatar da cewa sun kamu a ɗakunan gwajin cutar da ke asibitocin ƙasar.

Ta kuma ce alƙaluman ka iya sauyawa a kowanne lokaci sakamakon rahotonnin da ake samu a mabambantan wurare a faɗin ƙasar.

Cutar Kwalara ko amai da gudawa, cuta ce da ake kamuwa da ita sakamakon ɗaukar ƙwayar cutar ‘cholerae bacteria’, mutum kan kamu da cutar idan ya ci abinci ko ya sha ruwan da ke ɗauke da ƙwayar cutar.

Cutar dai kan zo da tsanani wanda a wasu lokutan ma take barazana ga rayuwar wanda ya kamu da ita, matuƙar bai samu kulawar gaggawa ba.

A wani labarin na daban kuma wani rahoto da hukumar daƙile yaduwar cutuka ta Najeriya NCDC ta wallafa a shafinta na intanet, ya nuna cewa an tabbatar da samun mutum 157 da ke ɗauke da cutar sankarau tsakanin watan Oktoban bara zuwa watan Maris da muke ciki.

Haka kuma an samu marasa lafiya da ake zargin sun kamu da cutar su kusan 628, ciki har da mutum 52 da suka mutu a jihohin ƙasar 21.

Alamomin cutar sun haɗar da zazzaɓi da ciwon kai da tashin zuciya da amai, da sanƙarewar wuya.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp