Ministan harkokin lantarkin, Inijiniya Abubakar D. Aliyu, ya kira taron gaggawa na masu ruwa da tsaki, domin samar da mafita dangane da matsalar wutar lantarkin Najeriya.
Taron ya kunshi kamfanonin samar da wutar lantarki da kuma hukumomi na gwamnati da masu zaman kansu da suke da ruwa da tsaki a harkar samar da wutar lantarki da iskar gas.
Taron, wanda aka gudanar a Abuja, Injiya Abubakar D. Aliyu ya ce, gwamnati ba za ta amince ba da yadda lamarin wutar lantarki ya samu koma baya, ya na mai cewa, dole a samo mafita ga dukkan matsalolin da suke kawo koma baya ga yawan wutar lantarki da ‘yan Najeriya suke samu a kullum.
Ministan ya kuma gargadi hukumomi da kamfanoni na harkar wutar lantarki su guji nunawa juna yatsa, su mayar da hankali wajen tallafawa juna wajen tabbatar da cewa ‘yan Najeriya suna samun isasshiyar wutar lantarki.
Taron ya mayar da hankali ne ga duba dukkan matsalolin da suke kawo koma baya ga harkar wutar lantarki a Nijeriya.
Injiniya Abubakar D. Aliyu ya ce, gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari, za ta ci gaba da kokarin daukar matakai, domin ganin cewa an samu karuwar wutar lantarkin da ake samarwa a Najeriya. In ji BBC.