fidelitybank

Ɗan shekaru biyu ya faɗo daga benen makaranta ya mutu

Date:

Iyaye sun shiga halin jimami yayin da ɗansu mai shekara biyu da wata shida ya faɗo daga ginin makaranta ya rasu a garin Aba da ke jihar Abia cikin kwanakin nan.

Rahotanni sun ce yaron mai suna David Udo, ɗalibin makarantar ‘Emerald International School’ da ke kan titin ‘Crystal Park’, Aba, ya faɗo daga saman bene mai hawa uku na makarantarsu.

An garzaya da yaron asibiti inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

A cewar iyayen yaron, wasu mutane ne da ba su sani ba suka kira su a wayar tarho suka shaida musu abin da ya samu yaron nasu a makaranta.

Mahaifin yaron mai suna John Udo wanda lauya ne ya yi zargin cewa har zuwa ranar Asabar shugaban makarantar bai kira su ya faɗa musu abin da ya faru da yaron nasu ba.

Da BBC ta tuntubi shugaban makarantar , Peter Nwoke, ya ce rahotonnin da aka bayar ba daidai ba ne, amma ya ki yin wani karin bayani kan abin da ya sani a kan lamarin. “Ba abin da ya faru ba ke nan,” in ji shi. “Idan kun zo ido da ido zan bayyana muku abin da na ji ya faru saboda ba na nan abin ya faru.”

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, Maureen Chioma Chinaka, ta shaida wa BBC cewa an samu korafi daga iyayen yaron kan abin da ya faru, kuma rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp