fidelitybank

‘Yan wasan Manchester United 12 sun ci gubar abinci a wasan Sherrif

Date:

‘Yan wasan Manchester United sun dawo daga kasar Moldova, inda suka kara da FC Sheriff a gasar cin kofin Europa a ranar Alhamis din da ta gabata wanda aka bayyana cewa ‘yan wasan sun ci gubar abinci, in ji jaridar UK Sun.

United ta samu nasara ne da ci 2-0 a balaguron farko da suka yi a kasar da ke gabashin Turai.

Kwallayen da Jadon Sancho da Cristiano Ronaldo suka zura a farkon rabin farko ya sanya kungiyar Erik ten Hag ta farfado daga rashin nasara da suka yi da Real Sociedad a gasar.

Sai dai kuma yanzu haka ya bayyana cewa, akalla ‘yan wasan 12 ne suka fara jinya bayan dawowar su da safiyar Juma’a.

United dai ta koma Birtaniya ne a wani jirgin sama mai zaman kansa bayan wasan, amma duk da haka ta kamu da wata cuta da ba a san ta ba, wadda ake kyautata zaton ta fito ne daga wani abu da suka ci, ko kuma daga jirgin da kansa.

Wasu Æ´an wasan sun rasa horon da aka shirya gudanarwa a ranar Juma’a a Carrington, yayin da wasu ke fama da rashin lafiya a washegari.

Godiya ga Ten Hag, ba dole ba ne ya shirya kungiyar don wasan gida da Leeds United, wanda aka shirya yi tun ranar Lahadi.

An dage wasan ne saboda karancin ‘yan sanda kafin jana’izar Sarauniyar a ranar Litinin a Westminster Abbey.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp