fidelitybank

‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane hudu a Katsina

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani rukunin gidaje masu tsada a Dutsen Reme a karamar hukumar Bakori a jihar Katsina a ranar Juma’a tare da yin garkuwa da mutane hudu.

An yi garkuwa da mutanen ne da misalin karfe 10 na dare a lokacin da ake ruwan sama.

Wata majiya daga Dutsen Reme ta shaidawa DAILY POST cewa ‘yan ta’addan sun aiwatar da haramcin nasu ne ba tare da kakkautawa ba.

Majiyar ta ci gaba da cewa, “mutanen kauye da ke kusa da Maska ne suka sanar da mu ta wayar tarho cewa ‘yan bindiga da dama sun nufo gidanmu, nan take muka sanar da ‘yan sanda da sojoji. Amma kafin isowarsu ‘yan bindigar sun riga sun yi garkuwa da mutane hudu.”

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da Bishir Shitu Sallau, ma’aikacin babbar kotun Funtua da wani Safiyanu dalibin kwalejin ilimi da ke Abuja.

A cewarsa, wadanda aka sace sun rigaya sun boye matansu a wani dakin wanka, inda ya kara da cewa “’yan fashin sun tafi da mazajen ne lokacin da ba su ga matan nasu ba, barayin sun nemi matansu.”

Majiyar ta bayyana cewa a rukunin da ake gudanar da aikin, ‘yan fashin sun yi awon gaba da wata Lauratu Jibril da ‘yar uwarta, bayan da mijinta, Malam Jibril, ya tsira da kyar.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp