fidelitybank

Tsohon gwamnan Kano zai jagoranci tawagar yaƙin neman zaɓen Osibanjo

Date:

Ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Yemi Osibanjo (OSO), ta naɗa tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafizu Abubakar, a matsayin shugaban ƙungiyar da zai jagoranci gangamin yaƙin neman zaɓen 2023.

An dai tabbatar da naɗin nasa ne tare da wasu shugabannin tafiyar, yayin wani taron ƙungiyar da ya gudana a Kano ranar Asabar.

Farfesa Hafizu dai shi ne mataimakin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga shekarar 2015 zuwa 2018.

Taron dai ya samu halartar kungiyoyin magoya bayan mataimakin shugaban ƙasar da suka fito daga sassa daban-daban na Najeriya.

Da yake jawabi yayin taron, Daraktan tsare-tsare na kungiyar, Bashir Suwaid, ya ce, akalla ƙungiyoyin da ke goyon bayan Osinbajo sama da 45 ne suka halarci taron.

Aminiya ta rawaito cewa, taron ya kuma zabi shugabanni daga dukkan shiyyoyin siyasa guda shida na ƙasar nan.

Sauran mukaman jagororin ƙungiyar sun hada da daraktan tsare-tsare da mai ba da shawara a bangaren shari’a da daraktan Kudi da na wayar da kan Jljama’a da na mulki da kuma na yaɗa labarai da dai sauransu.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp