fidelitybank

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu matafiya 12 a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato a hanyarsu ta zuwa ɗaurin auren ɗan’uwansu.

Ya buƙaci jami’an tsaro su tabbatar da kama masu laifin tare ganin an hukunta su.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkokin yaɗa labaru Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, shugaban ya ce ba za su lamunci aikata irin haka ba.

“Kowane ɗan ƙasa na da ƴancin yin tafiya zuwa kowane ɓangare na ƙasar nan,” in ji Tinubu.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe da kuma gwamnatin jihar Kaduna, inda ya yi kira da a kwantar da hankali tare da alkawarin cewa sai an hukunta maharan.

A ɗaya gefen, Tinubu ya nuna kaɗuwa kan mutuwar wasu mutum 10 da ƴar ƙunar bakin wake ta hallaka a babbar kasuwar kifi da ke karamar hukumar Konduga na jihar Borno ranar Asabar.

Ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga gwamnati da kuma al’ummar jihar kan lamarin da ya faru.

“Na bai wa jami’an tsaro umarnin matsa ƙaimi don farauto ƴan Boko Haram da suka rage don daƙile ayyukansu. Na kuma bai wa hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA umarnin tallafawa waɗanda abin ya shafa,” in ji shugaban Najeriyar.

Har ila yau, ya sake miƙa ta’azziyarsa ga mutum biyar da suka mutu a wata fashewa a jihar Kano.

Ya buƙaci hukumomi su gudanar da bincike don gano abin da ya haddasa fashewar tare da ɗaukar matakan da suka dace don kare afkuwarsa a gaba.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...
X whatsapp