fidelitybank

Ten Hag da wasu manya a Manchester sun ci amana ta – Ronaldo

Date:

Cristiano Ronaldo ya ce, Manchester United ta ci amanar sa yayin da ya ce, mai horas da kungiyar Erik ten Hag da wasu manyan jami’an gudanarwa na kokarin tilasta masa ficewa daga kungiyar a wata hira da aka yi da shi ranar Lahadi.

Dan wasan wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or sau biyar, ya kasance dan wasa a fili a United tun lokacin da Ten Hag ya karbi ragamar horar da ‘yan wasan a watan Mayu.

An ladabtar da Ronaldo ne bayan da ya ki zuwa maye gurbinsa a wasan da suka doke Tottenham da ci 2-0 a watan da ya gabata, amma ya koma taka leda a ‘yan makonnin nan, har ma ya zama kyaftin dinkungiyar a wasan da Aston Villa ta doke su da ci 3-1 a karshen makon jiya.

Sai dai dan wasan mai shekaru 37 ba ya cikin tawagar a wasan da United ta doke Fulham da ci 2-1 a wasan karshe na ranar Lahadi kafin hutun mako shida na gasar cin kofin duniya.

Ronaldo ya koma Old Trafford a watan Agustan 2021 daga Juventus.

Zamansa na farko a United ya kasance mai daukaka a karkashin jagorancin Alex Ferguson, inda ya lashe kofunan Premier uku, gasar zakarun Turai da kuma na farko na lashe kyautar Ballon d’Or a matsayin dan wasa mafi kyau a duniya.

Duk da kwallaye 24 da ya ci a duk wasannin da ya buga a kakar wasan da ta wuce, United ta sha fama da mummunan kamfen yayin da ta kare a matsayi na shida a gasar Premier kuma ta kasa tsallakewa zuwa gasar zakarun Turai.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp