fidelitybank

Sai Sojoji su fatattaki ƴanbindiga daga dazuka kafin a samu zaman lafiya – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce, dole sojoji su fatattaki ƴanbindiga su ƙwace dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen rashin tsaro.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ta’aziyar jaje ga Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago bisa rasuwar gomman mutane a sanadiyar gobarar fashewar tanka a jihar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A wata sanarwa da sakataren watsa labaran jam’iyyar APC na ƙasa, Edwin Olofu ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, Ganduje ya ce akwai buƙatar a ƙara ƙaimi, musamman wajen fatattakar ƴanbindiga daga dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen yaƙin harkokin ƴanbindiga a ƙasar.

“Hanyar da za a magance wannan matsalar ita ce a ƙwace dazuka saboda ƴanbindigar nan a cikin dazuka suke zama. Me ya sa muka koma muna jira su kawo hari, kafin mu tare su? lokacin da nake gwamna, kira na yi ga gwamnatin tarayya da ta zuba sojoji a dajin Falgore, wanda hakan ya sa aka kafa sansanin horar da sojoji.

“Tun daga lokacin ne aka fatattaki ƴanbindiga daga dajin, kuma Kano ta samu zaman lafiya,” in ji Ganduje.

Da yake mayar da martani, Gwamna Bago ya yi godiya bisa ziyarar jajen, sannan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gyare titin Suleja-Minna domin rage yawaitar haɗura.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp