fidelitybank

NNPP ta maka INEC a kotu a kan dan takarar Kaduna

Date:

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) reshen Jihar Kaduna ta maka Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) Kotu.

Tana neman a soke Sanata Uba Sani dan takarar gwamna na jam’iyyar APC bisa zargin tafka magudi a zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar 27 ga watan Mayun 2022.

Lokacin da aka gabatar da karar a gaban mai shari’a Hadiza R. Shagari ta babbar kotun tarayya da ke Kaduna a ranar Juma’a, dukkanin bangarorin sun nemi a kara musu lokaci domin su shirya su kuma mayar da martani ga bukatar.

Kungiyar lauyoyin NNPP ta samu jagorancin Mista Wole Agunbiade (SAN). APC tana da Barista Sule Shuaibu, yayin da lauyar INEC Barista Halima Gachi.

Don haka mai shari’a Shagari ya dage sauraron karar zuwa ranar 15 ga watan Satumba, 2022 domin sauraren karar.

Yayin da yake zantawa da manema labarai ta bakin wani dan kungiyar lauyoyin sa jim kadan bayan zaman kotun, Wole Agunbiade ya bayyana cewa suna son tabbatar da cewa hukumar zabe ta INEC ta yi abin da ya dace.

Ya ce bai kamata INEC ta wallafa sunan dan takarar ba saboda APC ba ta gudanar da sahihin zaben fidda gwani ba.

Ya jaddada cewa, “NNPP na kalubalantar zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da aka gudanar a ranar 27 ga Mayu, 2022.”

An ayyana Sanata Uba Sani ne a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC.

Ya samu kuri’u 1,149 ya zama wanda ya yi nasara, yayin da tsohon Mataimakin Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Abubakar ya samu kuri’u 37. Alhaji Mahmood Sani Shaaban ya samu kuri’u 10.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp