fidelitybank

Najeriya ta soke ziyarar Firaminista Fiala – Jamhuriyar Czech

Date:

Kafofin labaran Czech sun bayyana cewa, Najeriya ta soke ziyarar da firaministanta Petr Fiala ya shirya kai wa Abuja, babban birnin ƙasar ta Afirka ta Yamma.

Kakakin gwamnatin Jamhuriyar Czech Václav Smolka ya shaida wa jaridar Blesk ta Czech cewa, “Najeriya ta sanar da mu cewa ba ta iya samar da isashen shirin tarba da tsare-tsaren ziyarar firaminstan ba, don haka mun amince da soke ziyarar.”

Yayin da Najeriya ba ta ce uffan kan lamarin ba, wasu majiyoyin yaɗa labarai na kasar Czech sun nuna cewa wataƙila sokewar na da nasaba da goyon bayan da Czech ke baiwa Isra’ila a rikicin da ake fama da shi da kungiyar Hamas.

Czech dai tana cikin ƙasashen da suka kaɗa ƙuri’ar ƙin amincewa da ƙudurin Majalisar Dinkin Duniya na tsagaita buɗe wuta a rikicin Isra’ila da Hamas, yayin da kuma Najeriya ta amince da tsagaita buɗe wuta.

Fiala ya kai ziyara a yankin kudu da hamadar sahara daga makon da ya gabata don neman damar kasuwanci ga kamfanonin Czech.

Ya zagaya ƙasashen Habasha da Kenya, inda ya tattauna da shugabannin kasashen.

Ana sa ran zai gana da shugaban Ghana Nana Akufo-Addo a Accra a ranar Alhamis, kafin ya kammala ziyarar tasa a Ivory Coast a ranar Asabar.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp