fidelitybank

Najeriya da Poland sun kulla yarjejeniya a karo na farko

Date:

Najeriya da Poland a ranar Talata a Abuja, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna kan harkokin noma (MOU), inda kasar ta Turai ita ma ta yi alkawarin fadada fannin hadin gwiwar tattalin arziki a bangaren makamashi da masana’antu.

An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a lokacin ziyarar shugaban kasar Poland Andrezej Duda, wanda shi ne na farko da wani shugaban kasar Poland ya kai Najeriya, tun bayan kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu a shekarar 1961.

Da yake jawabi ga manema labarai tare da shugaban kasar mai ziyara, shugaba Buhari ya ce, Najeriya ta gamsu da hadin gwiwar da ake yi da kasar Poland a fannonin ruwa, ilimi da tsaro.

Dangane da harkokin noma, wanda daya ne daga cikin abubuwan da gwamnatin Najeriya ta sa gaba, shugaban kasar ya ce hadin gwiwa a wannan fanni zai zama nasara ga kasashen biyu, musamman ma a halin da ake ciki na karancin abinci a duniya da ake samu sakamakon rikicin Ukraine.

Ya yi nuni da cewa, daga cikin dimbin kalubalen da duniya ke fuskanta, Najeriya na son samar da sabbin hanyoyin yin hadin gwiwa da suka hada da tattaunawa kan dabaru akai-akai da tuntubar juna ta fuskar siyasa, ba wai kawai dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ba, har ma da magance batutuwan da suka shafi shiyya-shiyya da na kasa da kasa.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp