fidelitybank

Motar dakon mai ta fada rami a Ogun

Date:

Wata motar dakon mai dauke da man fetur, ta fada cikin wani rami a jihar Ogun.

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar, gabanin tashar Total, dake kan titin Sagamu/Ijebu-ode.

Motar tankar wadda ba ta da lambar rajista a cikinta, an ce ta rasa yadda za ta yi saboda gudun da ta yi; ya kauce daga hanya ya sauka cikin rami.

Domin kaucewa afkuwar wani hatsari na biyu ko kuma yiwuwar barkewar gobara, tuni hukumar FRSC da sauran jami’an tsaro suka killace yankin.

Kakakin hukumar FRSC a jihar Ogun, Florence Okpe, ta ce an karkatar da ababen hawa zuwa hanya daya.

Okpe ya kara da cewa, jami’an kashe gobara na nan a shirye domin kamo lamarin idan har wani abu ya faru.

Kalaman ta: “Hukumar kiyaye haddura ta tarayya, reshen jihar Ogun na son sanar da jama’a masu ababen hawa kan hatsarin da ya afku a safiyar yau, wanda ya shafi wata tankar da ba ta da lambar rajista a ciki.

“Motar ta rasa yadda za ta yi saboda gudun da ya wuce kima, ta fada cikin rami, cike take da PMS.

“Ma’aikatan kashe gobara suna kan kasa. An killace wurin don taka tsantsan da kuma gujewa karo na biyu. An karkatar da zirga-zirga zuwa ɗayan layin. Jami’an hukumar FRSC suna nan a kasa suna kula da lamarin.

“An shawarci masu ababen hawa da su tuÆ™i a hankali tare da ba da haÉ—in kai tare da masu kula da zirga-zirgar ababen hawa da ke kula da lamarin.”

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp