fidelitybank

Mayakan Tigray a Habasha sun kwace iko da yankin Kobo

Date:

Rahotanni daga Ethiopia na cewa ana ci gaba da yaƙi a yankin Amhara da ke arewacin ƙasar bayan rushe tsagaita wutar da aka yi na tsawon wata biyar a makon jiya.

Mayaƙan Tigray sun ƙwace iko da garin Kobo da ke yankin Amhara bayan da suka nausa Kudancin ƙasar kusa da kan iyaka.

Mazauna garuruwa da ƙauyuka da suka tattauna da BBC sun ce an ci gaba da faɗa a cikin tsaunukan da ke kusa dasu kuma kamar baza a daina ba.

A halin yanzu hukumomi a Woldia da Dessie- manyan garuruwan Amhara biyu da ke kusa da yankin sun ƙaƙaba taƙaitacciyar dokar hana fita da daddare.

Gwamnatocin Oromia da yankin Somali da ke gabashi sun bayyana goyon bayansu ga sojoji da yankunan Amhara da na Afar da ke fuskantar sabbin hare-hare.

A lokacin da ake ganiyar yaƙi a bara, yankuna da dama sun aika sojoji zuwa filin daga.

Akwai zarge-zarge da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta cewa faɗa na iya dawowa kan iyakokin Tigray da Eritrea mai maƙwabtaka.

Babban jami’in Tigray Getachew Reda ya yi ikirarin cewa jami’an rundunar sojin Habasha sun tsallaka kan iyakoki domin haɗa kai da Eritrea.

Zuwa yanzu dai BBC bata tabbatar da wannan ikirari ba.

Firamnista Abiy Ahmed wanda har yanzu bai fito fili ya yi magana ba tun bayan dawowar yaƙin, ya kai wata ziyarar aiki zuwa Algeria.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp