fidelitybank

Majalisar Kolin shari’ah ta yi tir da Tinubu a kan tsadar rayuwa

Date:

Majalisar koli ta shari’ah a Najeriya, ta yi tir da shugaba Bola Ahmed Tinubu kan matsalar tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.

Shugaban Majalisar, Sheikh AbdurRasheed Hadiyatullah ne ya bayyana hakan a wani taro da aka yi a Abuja ranar Talata.

A cewarsa, wahalhalun da ‘yan Najeriya ke ciki ya karu a karkashin Tinubu, sakamakon hauhawar farashin kayayyakin abinci da kayayyaki da kuma ayyuka a fadin kasar.

“Wahalhalun da ‘yan Najeriya ke fama da su ya ta’azzara tun lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki.

“Abin da ake sayar da shi N200 yanzu ana sayar da shi akan N2,000. A halin yanzu Najeriya na fama da karancin kudi, rashin aikin yi, da kalubalen tattalin arziki,” in ji shi.

Hauhawar farashin kayan abinci ya karu zuwa kashi 28.92 da kuma kashi 33.93 bisa 100, a watan Disambar 2023, a cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa.

A halin da ake ciki kuma, wani kwararre kan harkokin kudi, Okechukwu Unegbe, tsohon shugaban Cibiyar Banki ta Chartered, ya shaida cewa hauhawar farashin kayayyaki a kasar ya haura kashi 40 cikin dari.

Wannan na zuwa ne watanni bayan cire tallafin man fetur da kuma hauhawar farashin Naira a watan Yunin 2023.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp