fidelitybank

Majalisar Dokokin Ribas za ta kara tantance tsofaffin kwamishinonin da suka ajiye aiki

Date:

A yau ne Majalisar Dokokin Jihar Ribas karkashin jagorancin Martins Amaewhule za ta sake tantancewa tare da tabbatar da sunayen kwamishinoni tara.

Kwamishinonin dai su ne wadanda suka yi murabus daga nadin nasu sakamakon zazzafar rikicin siyasar jihar tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike da kuma wani sashe na Majalisar karkashin jagorancin Amaewhule.

An yi imanin matakin da Majalisar ta dauka ya yi daidai da kudurori guda takwas da Fubara, Wike, da wasu manyan shugabanni suka rattabawa hannu kan rikicin siyasar jihar, bayan shiga tsakani na Shugaba Bola Tinubu.

Wani bangare na kudurin shi ne cewa a sake nada kwamishinonin da suka yi mulki.

Sai dai babu tabbas ko sunayen kwamishinonin gwamnan ne ya aika majalisar domin tantancewa da tabbatarwa ko kuma ‘yan majalisar na yin nasu ne.

A halin da ake ciki, Gwamna Fubara a jiya ya rantsar da sabbin Sakatarorin Dindindin 16 don gudanar da ayyukan gudanarwa na ma’aikatun, “har sai lokacin da ma’aikatun za su sami shugaban siyasa.”

Gwamnan ya kuma bayyana cewa nadin nasu ba siyasa bace.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp