fidelitybank

Kungiyoyin Kwadagona ganawa da Gwamnati kan man fetur

Date:

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago biyu, za su gana da jami’an gwamnati don kokarin ganin sun amince da sabon mafi karancin albashi da kuma wasu bukatu na ma’aikata bayan da Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur.

Janye tallafin ya jawo tashin farashin mai da tsadar sufuri.

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC a Najeriya ta ce yau ne wa’adin da ta ba gwamnatin tarayya ke cika, kan bukatarta mayar da mafi karanci albashi naira dubu 200 sakamakon janye tallafin mai.

Ƙungiyar ta ce bukatar biyan mafi kakantar albashin naira dubu 200 na cikin bukatun da ta mika wa gwamnatin Tarayya, domin ragewa ma’aikata raɗaɗin wahalar janye tallafin mai da sabuwar gwamnatin ta yi.

Comrade Nuhu Toro, sakatare janarar da kungiyar ya faɗawa BBC cewa suna kan bakansu akan albashi mafi ƙanƙanta na naira dubu 200 wa ƙaramin ma’aikaci a Najeriya domin tsadar rayuwar da mutane suka shiga.

Ya ce “Farashin kayayyaki da rayuwa ma gaba daya tsada ya keyi, saboda haka gwamnati ba ta da hujja illa ta ƙara ma ma’aikata mafi ƙanƙantar albashi na naira dubu 200 domin su ma’aikata su suke ƙirƙirowa ta arzikin ƙasa”.

“Gwamnati za ta iya biyan wannan albashin idan ta rage almubazaranci, idan ta rage sama da faɗi da dukiyan talakawa, kuma idan ta rage kashe kuɗi a kan abubuwan da bai kamata ba.”

Toro ya dai ƙara da cewa dole ne gwamnati ta rage yawan kashe kudin da take yi, shi ne za ta sami yanda za tayi ta biya ma’aikata albashi mafi ƙanƙanta naira dubu 200.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp