fidelitybank

Knugiyoyin Dattawan Arewa da na Inyamurai sun soki Tinubu a kan tafiye-tafiye

Date:

Kungiyar dattawan arewacin Najeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al’ummar Igbo da wasu kungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin dadinsu game da tafiya zuwa Paris da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da kasar ke fama da karuwar matsalar tsaro.

A ranar Laraba 24 ga watan Janairu ne shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta kashin kai.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Najeriya cikin makon farko na watan Fabarairu.

Sai dai kungiyoyin a hirarsu da jaridar Daily Trust sun koka cewa babu gaskiya cikin sanarwar tafiyar la’akari da yadda aka kira tafiyar ta “kashin kai”.

Matakin kungiyoyin na zuwa ne bayan da shi ma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya soki Tinubu inda ya bayyana shakku game da makasudin tafiyar tasa zuwa Faransa yayin da ake fuskantar karuwar matsalar yan bindiga da sauran matsalolin tsaro da ke ci gaba da ta’azzara.

Sai dai Fadar shugaban kasar ta ce duk da cewa Tinubu ba ya kasar, yana aiki tukuru domin kawo saukin matsalolin kuma yana bai wa hukumomin tsaro dukkanin goyon bayan da suke bukata domin samun nasara kan masu aikata miyagun laifuka da nufin fitar da Najeriya daga halin rashin tsaron da take ciki.

Tinubu dai ya sa kafa ya fice daga kasar yayin da ake tsokaci game da jerin hare-haren da aka kai a Filato da sace-sacen jama’a a Abuja, babban birnin kasar da kuma hari na baya-bayan nan na sace dalibai da malaman makaranta a jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin Najeriya.

Kungiyar dattawan arewacin Najeriyar ta ce tafiyar ta Tinubu zuwa Paris a irin wannan yanayi da ake ciki a kasar manuniya ce cewa shugaban ya dukufa ne wajen cimma kudurorinsa na kashin kai a maimakon bai wa yan Najeriya kwarin gwiwa a lokacin da suke bukatar hakan.

Daraktan yada labarai na kungiyar, Abdulazeez Sulaiman ya ce kungiyar tana ganin matakin na shugaban kasar na tabbatar da damuwar da ake nunawa cewa Najeriya ta fada cikin matsalar rashin shugabanci na gari da rashin nuna damuwa da tausayi.

A nata bangaren, kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta yi allah-wadai da tafiyar ta shugaba Tinubu zuwa Paris a halin tabarbarewar tsaro da sauran kalubale da ake ciki.

Babban sakataren kungiyar, Mazi Okechukwu Isiguzoro ya ce bulaguron da Tinubu ya yi na zuwa ne a lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen tattalin arziki.

Isiguzoro ya yi kira ga Tinubu da ya yi wa yan Najeriya bayani dalilin yin irin wadan nan tafiye-tafiye.

Shi ma shugaban kungiyar tabbatar da jagoranci na gari, GGT, Mista Tunde Salman ya ce da alama shugaba Tinubu ya bai wa wasu manyan jami’ai har da mataimakin shugaban kasa damar tafiyar da al’amuran.

Ya ba da misali da wani kwarya-kwaryan taro da aka shirya kan tsaro game da karuwar matsalar a arewacin Najeriya, inda mataimakin shugaban kasa da ministocin tsaro suka zama masu taka rawa sosai a taron.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp