fidelitybank

Hisbah ta ƙwace kwalaben giya 1,906 a Jigawa

Date:

 

Hukumar Hisbah ta Jihar Jigawa ta ce ta ƙwace kwalabe 1,906 na barasa iri-iri a sintiri daban-daban da ta gudanar a jihar a 2021.

Kwamandan Hisbah na jihar, Ibrahim Dahiru ya baiyana haka a lokacin da ya ke zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a Dutse a yau Talata.

Dahiru ya ce an ƙwace waɗannan kayan mayen ne a lokacin da jami’an Hisbah su ka kai samame a wuraren shaye-shaye da otal-otal da ke jihar.

Ya ce an kama waɗanda a ke zargi da karuwanci su 92, inda ya ce an damƙe su ne sakamakon aikata baɗala.

“An kama waɗanda ake zargin da aikata lalata da suka hada da caca, karuwanci na shirya raye-raye a lokacin bukukuwan aure da sauransu.

“Har ila yau, hukumar ta samu damar rufe gidajen karuwai a fadin jihar a cikin lokacin da ake nazari,” in ji shi.

Dahiru, wanda ya nanata cewa an haramta shan barasa a tsakanin musulmi masu kishin jihar, ya kuma bukaci mazauna jihar da su guji aikata ayyukan lalata da sauran munanan dabi’u da ke iya lalata al’umma.

Ya kuma ƙara da cewa, an miƙa su ga ‘yan sanda wadanda aka kwace da kuma wadanda ake zargin ga ‘yan sanda domin ci gaba da daukar mataki.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp