fidelitybank

Hamas ta naɗa Yahya Sinwar a matsayin sabon jagoran siyasar ta

Date:

Tun a 2017 Sinwar ya taɓa riƙe muƙamin jagoran ƙungiyar a Zirin Gaza, a yanzu kuma ya zamo shugabanta.

Shugabannin Hamas baki ɗaya suka amince a naɗa Sinwar domin shugabantar kungiyar, kamar yadda wani babban jami’in Hamas ɗin ya shaidawa BBC.

Sanarwar ta zo a daidai lokacin da ake zaman fargaba a Gabas ta Tsakiya yayin da Iran da ƙawayen ta suka yi barazanar ɗaukar fansa kan kisan Haniyeh, wanda ta zargi Isra’ila da aikatawa. Har yanzu dai Isra’ila ba ta ce komai a kai ba.

A yayin zaman tantance sabon shugaban Hamas ɗin a Doha, an gabatar da sunan Yahya Sinwar da kuma Mohammed Hassan Darwish.

Talla

Daga nan ne jagororin ‘’suka yi tarayya baki ɗayan su wajen zaɓen Sinwar,’’ inji wani babban jami’in ƙungiyar.

Jami’in ya ƙara da cewa “Sun kashe Haniyeh, wani mutum mai sauƙin kai wanda ya yarda da bin hanyar sulhu wajen samar da mafita. A yanzu za su yi fama da Sinwar da kuma jagororin sojojin Hamas.’’

Kafin mutuwar sa dai, masana diflomasiyyar yankin suna yi wa Ismail Haniyeh kallon mai sassauci da sauƙin kai a tsakanin sauran jagororin Hamas, kuma shi ne kan gaba wajen shiga tattaunawar sasanici da ƙungiyar.

Shi kuwa Yahya Sinwar, ana yi masa kallon ɗaya daga cikin masu tsattsauran ra’ayi a cikin shugabannin ƙungiyar.

Yanzu haka dai Sinwar ne mutumin da Isra’ila ke nema ruwa a jallo. Jami’an tsaron Isra’ila sun jajirce cewa shi ne ya kitsa harin ranar bakwai ga watan Oktoban 2023, wanda ya kashe mutane fiye da 1,200, kuma Hamas ta yi garkuwa da wasu 251 daga cikin su.

Tun bayan harin na watan Oktoban bara ba a ganin Sinwar a fili, kuma ‘’ya ɓoye ne a cikin wani ginin ƙarƙashin ƙasa’’a Gaza, inji sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken.

An haifi Sinwar ne a wani sansanin ƴan gudun hijira a Khan Younis, a 1962.

A 1980, Sinwar ya kafa rundunar tsaron Hamas, wadda aka fi sani da Majd, kuma an yi zargin cewa ita ce ta riƙa bibiyar Falasɗinawa masu goyon bayan Isra’ila.

Ya shafe mafi yawan rayuwarsa a gidan yarin Isra’ila, kuma bayan kamu na uku da aka yi masa a 1988, sai aka yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai a gidan yari.

Sai dai kuma ya samu kansa a cikin Falasɗinawa 1,027 da Isra’ila ta saka a 2011, lokacin wata musayar fursunoni, inda aka miƙawa Isra’ila Gilad Shalit wani soja da Hamas ta tsare na tsawon fiye da shekara biyar.

A 2017 aka naɗa Sinwar mai shekara 61, a matsayin shugaban sashin siyasa na ƙungiyar Hamas, kuma tun daga lokacin yake riƙe da muƙamin har zuwa yanzu da aka bashi jagorancin kungiyar.

Amurka ta sanya sunan Sinwar a jerin sunayen ƴan ta’adda na duniya.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp