fidelitybank

Gwamnatin Tinubu na buƙatar addu’ar ku – Yari

Date:

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdul’aziz Yari, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu addu’a, a lokacin bukukuwan Sallah.

Yari ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke garin Talata-Mafara a yankin Talata-Mafara a jihar.

Ya kuma bukaci daukacin ‘yan Nijeriya, ba tare da la’akari da kabilanci da bambance-bambancen yanki ba, da su yi wa Tinubu addu’ar samun nasara.

A cewar Yari: “Ya kamata mu yi addu’a ga Allah ya yi mana jagora da goyon bayan zababben shugaban kasar mu don aiwatar da ci gaba mai ma’ana ga ‘yan Najeriya.

“Mun yi imani da Tinubu, muna da yakinin karfinsa na gina Najeriya.

“APC a matsayin jam’iyya tana da tsare-tsaren gina Najeriya.”

Daga nan sai ya yi kira ga ‘ya’yan jam’iyyar APC da su kwantar da hankalinsu da bin doka da oda.

Yari ya bukaci mazauna jihar da su marawa gwamnatin jihar baya.

“Ina amfani da wannan kafar domin yin kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da ba gwamnati goyon baya a dukkan matakai da hukumomin tsaro domin magance matsalolin tsaro.

Yari ya ce “Ya kamata a bar hukumomi su yi aikinsu don magance matsalolin tsaro da ke fuskantar al’ummominmu.”

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp