Ministan harkokin sadarwa, Farfesa Ali Isa Pantami, ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya zuwa Kano, domin mika ta’aziyyar ta ga iyalan shahararren malamin addinin Islama, Dr Ahmad Ibrahim (BUK).
Dr. Ahmad mai shekaru 82 ya rasu a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano, bayan gajeruwar rashin lafiya.
Tawagar gwamnatin tarayya da ta samu wakilcin, Alhaji Lai Mohammed, Ministan yada labarai, sun isa masallacin marigayin inda suka mika sakon ta’aziyar su ga ‘yan uwa da abokansa suka tarbe shi.
Da yake gabatar da tawagar, mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu, wanda ke cikin tawagar, ya ce, shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne ya aiko su, domin yin ta’aziyya ga iyalai da kuma al’ummar Kano baki daya.
Shugaban tawagar Pantami, ya ce, rasuwar malamin babban rashi ne ga al’ummar kasar, inda ya ce ya bar wa al’ummar kasar tuwo a kwarya.
Ya yi addu’ar Allah ya jikansa da rahama, ya kuma baiwa iyalai, dalibansa da kuma abokan zamansa karfin gwiwa ta hanyar rashin.
Da ya ke jawabi a madadin ‘yan uwan marigayin, babban limamin masallacin BUK, Dr. Abubakar Jibrin, ya gode wa shugaban da tawagar bisa wannan ziyarar.
School