fidelitybank

Fasinja ya dabawa direba wuka har lahira

Date:

Wani mutum mai suna Akpa Lebechukwu daga jihar Enugu ya dabawa wani direban bas wuka ya mutu har lahira a jihar Anambra.

DAILY POST ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a Junction Okija, karamar hukumar Ihiala ta jihar Anambra, inda direban da ke dawowa daga Legas, kuma ya nufi jihar Imo ya yi fakin domin sauke wasu fasinjoji.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Anambra, DSP Toochukwu Ikenga, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwar manema labarai da aka rabawa manema labarai, ya ce, mutumin ya shiga motar ne bayan da direban ya sauke fasinjoji tare da daka masa tsawa.

Ikenga ya ce: “A Lahadi 18/9/2022 da misalin karfe 12:05 na rana, ‘yan sanda sun kama wani Akpa Lebechukwu ‘M’ dan shekara 25 daga jihar Enugu, kuma sun kwato masa adduna daya.

“Wanda ake zargin ya kai hari kan direban wata motar kasuwanci da ke kan hanyar Legas zuwa jihar Imo a mahadar Okija, kan titin Onitsha/Owerri.

“Wanda aka kashe ya ajiye fasinja domin sauke fasinja kafin Lebechukwu ya shiga cikin motar ya daba wa direban daba. An garzaya da direban asibiti kafin wani likita da ke bakin aiki ya ce ya mutu.”

Sai dai ba a bayyana mene ne manufar maharin ba, haka kuma ba a tabbatar da lafiyarsa ba.

Ikenga ya ruwaito kwamishinan ‘yan sandan jihar Anambra yana bada umarnin mika lamarin ga hukumar binciken manyan laifuka ta jihar.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp