fidelitybank

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Date:

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta fitar da rahoton saukar hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya, jihohi goma tare da babban birnin Tarayya, Abuja na ci gaba da fama da hauhawar farashi da ya haura kashi 30 cikin 100.

Wannan na nuna alamar cewa matsin tattalin arziki na ci gaba da gallaza wa al’umma a wasu sassan ƙasar.

Rahoton hauhawar farashi na wata-wata ya nuna cewa a watan Afrilun 2025 hauhawar farashi ya sauka zuwa kashi 23.71 cikin 100 idan aka kwatanta da kashi 24.23 cikin 100 a watan Maris da kuma kashi 33.69 cikin 100 a watan Afrilu na bara.

Sai dai duk da saukar farashin a matakin ƙasa, jihohin Enugu da Kebbi da Neja da Benue da Ekiti da Nassarawa da Zamfara da Delta da Gombe da Sokoto da kuma Abuja har yanzu suna fuskantar hauhawar farashi kayayyaki.

Jihar da ta fi fuskantar hauhawar farashi mafi muni ita ce Enugu inda ya kai kashi 36.0 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Na Kebbi da Niger ya kai kashi 35.1 da 34.8 cikin 100 bi da bi.

Farashin abinci na ci gaba da ƙara tsananta rayuwar jama’a a waɗannan jihohi.

A Jihar Benue, hauhawar farashin abinci ya kai kashi 51.8 cikin 100 idan aka kwatanta da bara, tare da ƙarin kashi 25.6 cikin 100 a cikin wata guda.

Wannan na da nasaba da rashin tsaro da ke kawo cikas ga noman abinci in ji rahoton.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp