fidelitybank

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan ta’adda sun sako mutane 60 da su ka ɗauke a coci a Kaduna

Date:

 

Bayan wata ɗaya a hannun masu garkuwa da mutane, masu bauta a cocin emanuel baftis da ke Kakau Daji, Jihar Kaduna sun shaƙi iskar ƴanci.
A ranar 31 ga watan Oktoba ne dai masu ibadar su na tsaka da bauta a cikin cocin, sai ƴan yadda su ka dirar musu, inda su ka yi awon-gaba da mutum 60 da ga cikin su.
Bayan ƴan kwanaki, sai ƴan ta’addan su ka hallaka uku da ga ciki sannan su ka kaiwa biyu munanan raunuka bayan sun nemi a basu kuɗin fansa.
Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasar, reshen Jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab ne ya baiyana sakin masu bautar a yau Asabar.
Ya ƙara da cewa a kwai wasu mutane 9 ma da a ka sake su tare da ƴan cocin a jiya Juma’a da daddare.
Sai dai kuma Hayab bai baiyana cewa ko sai da a ka biya kuɗin fansa sannan a ka saki masu bautar ba, ya ce dai kawai ma’aikatan cocin ne su ka sanar da shi sannan sojoji sun tafi da su bariki.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp