Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan kasafin kudin shekarar 2022 na Naira Tiriliyan 17.126.
Shugaban ya rattaba hannu kan kasafin kudin kasar ne a ranar Juma’a a zauren majalisar da ke fadar shugaban kasa da ke Abuja, babban birnin tarayya.
Babban mai taimaka masa na musamman a majalisar dattijai kan harkokin majalisar dokoki ta kasa, Sanata Babajide Omoworare ne ya gabatar wa shugaban kasa kudirin kasafin kudin.
Yayin da shugaba Buhari ya rattaba hannu a kan kasafin, shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ne su ka mara masa baya.
Ministar kudi da kasafin Kudi da tsare-tsare takKasa, Mrs Zainab Ahmed, ita ma ta shaida rattaba hannu kan kasafin kudin.