fidelitybank

Atiku zai karɓi Shekarau a Kano bayan ya koma PDP daga NNPP

Date:

A yau ne ake sa ran dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar zai tarbi Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya, Ibrahim Shekarau, ya dawo PDP.

Idan za ku tuna, Shekarau da ya koma jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a farkon wannan shekarar, ya fice daga jam’iyyar ne a kwanaki kadan da suka gabata, saboda rashin jituwar da ake yi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Sanata Rabi’u Kwankwaso.

Tsohon Gwamnan Kano wanda aka zaba a matsayin Sanata a Jam’iyyar APC, ya bar Jam’iyyar ne tun da farko, bayan da suka yi taho-mu-gama da Gwamna Abdullahi Ganduje.

Shugaban PDP na jihar Kano Shehu Wada Sagagi ya shaida wa Aminiya cewa, Shekarau ya amince ya koma babbar jam’iyyar adawa kuma da fatan za a karbe shi a yau.

Ya ce, “Alhamdulillah, daga karshe mun samu shugaba a Kano, na ji dadi. Shekarau a matsayinsa na babban mai rike da mukamai na siyasa kamar yadda tsarin mulki ya tanada, ya yarda kuma mun yi masa maraba da komawa jam’iyyarmu ta PDP.

“Duk shirye-shirye sun yi nisa a shirye-shiryen tarbar Atiku Abubakar da zai zo Kano ranar Lahadi, da fatan zai tarbi Mallam Ibrahim Shekarau. Mun yarda mu bi shi kuma za mu yi nasara in Allah Ya yarda.”

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp