Gwamna jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya ce, ya fadawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar cewa, kada ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023.
Naija News ta rawaito cewa, Mohammed ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a lokacin da kwamitin tuntuba da juna da ya kafa domin neman shugabancin kasar ya mika masa rahotonsa.
Gwamnan Bauchi ya ce, Atiku ya tsufa da yawa, kuma ba zai iya shugabancin kasar nan ba, inda ya nemi jigon jam’iyyar PDP da ya goyi bayan aniyarsa ta zama shugaban kasa a 2023.
Gwamnan, ya yi alkawarin marawa tsohon mataimakin shugaban kasar baya idan ya zama dan takarar jam’iyyar kuma ‘yan Najeriya sun fifita shi fiye da sauran masu neman takara.