fidelitybank

Ambaliya: Gwamnatin Jigawa ta hada hannu da Netherland – Badaru

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta hada hannu da kasar Netherland domin dakile matsalar ambaliyar ruwa da ta addabi wasu sassan jihar.

Gwamna Mohammed Badaru Abubakar ya bayyana haka ne a jiya a lokacin da ya karbi bakuncin kwararru kan yadda za a shawo kan ambaliyar ruwa daga kasar Netherlands a ofishinsa da ke Dutse.

Ya yi bayanin cewa gwamnatin jihar Jigawa ta hada gwiwa da kwararrun domin samar da mafita mai dorewa ga matsalar ambaliyar ruwa da ta addabi jihar a duk shekara.

A cewarsa, kasar Netherlands tana da tarihin gudanarwa da sarrafa ambaliyar ruwa sama da shekaru 300.

“Muna bukatar mafita don kawo karshen asarar rayuka da dukiyoyi da ake yi duk shekara da kuma ganin yadda za a canza ruwa zuwa fa’idar tattalin arzikin Jihar,” in ji Badaru.

Gwamna Badaru ya ce “Za a shawo kan ambaliyar kuma a ajiye ruwan domin a yi amfani da shi wajen noman noman rani.”

DAILY POST ta ruwaito cewa, gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da kwamitoci guda biyu masu karfi domin dakile illolin ambaliyar ruwa a jihar.

Sama da mutane 133 ne suka rasa rayukansu da dukiyoyin da ya kai Naira tiriliyan 1.5 a ambaliyar ruwa ta bana a fadin Jihar.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp