fidelitybank

AFCON: Habasha ce ta farko da ta fara halartar kasar Kamaru

Date:

Kasar Habasha ita ce ta farko da ta isa kasar Kamaru, domin buga wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afirka na mai taken TotalEnergies 2021, wanda za a fara ranar 9 ga watan Janairun 2022.

Tawagar ta isa filin jirgin saman Nsimalen na Yaounde a ranar Lahadi 26 ga Disamba.

Bayan isowar, ‘yan wasa, ma’aikatan fasaha da masu zartarwa na FA sun yi gwajin Covid-19 a filin jirgin sama kafin su koma otal din kungiyarsu.

Kocin kasar, Wubetu Abate da tawagarsa sun yi atisaye a filin wasa na Ahmadou Ahidjo Annex 1.

Walias sun dawo gasar a karon farko tun 2013. Wanda su ka taba lashe gasar kofin AFCON guda daya, da a ka gudanar a shekarar 1962 a kasar ta.

Habasha ta na cikin rukunin A ne da Burkina Faso da Cape Verde da Kamaru mai masaukin baki.

A ranar 9 ga watan Janairu ne za su kara da Cape Verde bayan wasan farko tsakanin Kamaru mai masaukin baki da Burkina Faso. Habasha za ta kara da mai masaukin baki ne a ranar 2 ga wata kafin a rufe wasannin rukuni-rukuni da Burkina Faso a ranar 17 ga watan Janairu.

 

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp