fidelitybank

Ɗalibai 30 da malami 1 sun shaƙi iskar ƴanci a Kebbi

Date:

Ƴan bindiga sun sako wasu ɗalibai 30 da wani malami 1 na makarantar Kwalejin Yauri da ke jihar Kebbi.

Sanarwar da mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kebbi kan harkokin yada labarai, Yahaya Sarki ya aike wa manema labarai, ta ce, tuni a ka mika su ga hukumomin lafiya, domin duba lafiyarsu, kuma daga bisani za a sada su da iyayensu.

Shi ma mai bai wa gwamnan jihar shawara kan sha’anin tsaro Garba Rabi’u, ya shaida wa BBC cewa an kubutar da daliban ba tare da an biya kudin fansa ba, ya na mai cewa suna cikin koshin lafiya.

Sai dai ya ce har yanzu akwai sauran daliban da ke hannun ‘yan bindigar, wadanda su ma a ke sa ran kubutar da su nan ba da jimawa ba, a cewar hukumomi.

Rahotanni na nuni da cewa, tun a watan Yunin bara ne dai Ƴan bindigar su ka sace su, wanda a yanzu su ka shaƙi iskar ƴanci.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp