Gwamnatin Jihar Kebbi ta tabbatar da kuɓutar ɗaliban Makarantar Gwamnatin Taraiya Birnin Yauri, waɗanda ƴan ta’adda su ka yi garkuwa da su tun a shekarar da ta gabata.
Yahaya Sarki, mai baiwa Gwamna Atiku Bagudu shawara ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Birnin Kebbi a jiya Asabar.
Ya ce ” yau 8 ga watan Janairu, 30 da ga cikin ɗaliban Makarantar Gwamnatin Taraiya ta Birnin Yauri da mamaki 1 sun kuɓuta kuma tuni sun iso Birnin Kebbi.
“Za a duba lafiyar su da kuma tallafa musu yayin da za a sada su da iyalan su.
“Yayin da mu ke taya Shugaban Ƙasa murna, mu na kuma godewa jami’an tsaro da sauran waɗanda su ka bada gudunmawa wajen sakin ɗaliban,” in ji sanarwar.
A tuna cewa a ranar 22 ga watan Oktoban 2021 a ka saki 30 da ga ɗaliban makarantar, gami da wadanda kafin nan a ka sake su.